play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right ‘Yan Bindiga Sun Sace Faston Cocin Katolika Da Mai Girkinsa a Kaduna

Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Faston Cocin Katolika Da Mai Girkinsa a Kaduna

Bello Sani March 31, 2021 5


Background
share close

Ƴan bindiga sun sace faston cocin katolika da wasu mutane a daren ranar Litinin Kaduna

Yan bindiga sun sace, Mista Anthony Dawah, Faston Cocin Katolika, mai masa girki, da matar wani mai koyar da sabbin wadanda suka karbi addinin kirista ibada a ƙauyen Kushe Makaranta a ƙaramar hukumar Kagarko a jihar Kaduna.

Lamarin ya faru ne misalin ƙarfe 2 na daren ranar Litinin a lokacin da ƴan bindigan suka kai hari a garin, rahoton The Cable.

Lamarin na zuwa ne bayan kwanaki takwas da sace mambobin cocin RCCG takwas a ranar Juma’a a hanyar Kaduna zuwa Kachia.

Mista Joseph Hayab, shugaban Kungiyar Kiristocin Nigeria ta CAN a jihar ya tabbatar wa majiyar Legit.ng afkuwar lamarin.

“An sace Reverend Fada Dawah misalin ƙarfe 2 na daren Litinin tare da mai masa girki da matar mai koyar da sabbin wadanda suka karbi addinin kirista da wasu mutane,” in ji Hayab.

“Har yanzu yana hannun yan bindigan kuma ba su kira sun faɗa inda suke ba,” ya ƙara da cewa.

Muhammad Jalige, kakakin rundunar yan sandan jihar bai ɗaga wayansa ba a lokacin da aka kira shi.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *