play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right ‘Yan bindiga sun ‘sace ɗalibai da dama’ a makarantar sakandaren Ƙanƙara

Labarai

‘Yan bindiga sun ‘sace ɗalibai da dama’ a makarantar sakandaren Ƙanƙara

Bello Sani December 12, 2020 12


Background
share close

Rahotanni daga jihar Katsina da ke Najeriya sun ce ‘yan bindiga sun kai hari a makarantar sakandaren kimiyya da ke garin Ƙanƙara inda suka sace ɗalibai da dama.

Rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar wa BBC kai harin ranar Juma’a da daddare, amma ta ce ba ta da bayanai kan sace ɗaliban.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Gambo Isa, ya shaida mana cewa tuni aka gano ɗalibai fiye da 200 da suka tarwatse suka shiga cikin daji lokacin da ‘yan bindigar suka auka wa makarantar tasu.

Ya ƙara da cewa an yi ba-ta-kashi tsakanin ‘yan bindigar da ‘yan sanda lamarin da ya kai ga “harbin ɗan sanda ɗaya amma bai mutu ba.”

A cewarsa, an tura ƙarin ‘yan sanda domin su far wa ‘yan bindigar yana mai cewa kawo yanzu suna ci gaba da ƙirga ɗaliban da suka koma makarantar daga daji a kuma waɗanda ba su dawo ba domin sanin ainihin yawan waɗanda aka sace.

Sai dai wani ganau ya shaida wa BBC cewa an sace ɗalibai da dama a harin da ‘yan bindigar suka kai.

Mutumin, wanda ba ya so mu ambaci sunansa, ya ƙara da cewa: “A gabana ‘yan bindigar suka wuce suna harbe-harbe suka shiga makarantar kuma sun sace ɗalibai da dama. Tun da yamma muka samu labarin cewa za su kawo hari kuma mun shaida wa jami’an tsaro amma ba a ɗauki mataki ba.”

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *