
EFCC ta Kama Mahaifiya da Ɗanta kan Damfara ta Intanet a Legas
Jami’an hukumar yaki da masu almundahar kudi ta EFCC ta kama Ibeh Theophilus Uche, Shugaban 10 Kobo Wine Place da ke Ikotun a Legas tare da mahaifiyarsa kan zarginsa da […]
Gaba Tsakanin Makota Bello Sani
Akalla mambobin Cocin Redeemed Christian Church of God takwas yan bindiga suka sace a Kaduna, a ranar Juma’a, 26 ga watan Maris.
Jaridar The Punch ta rahoto cewa wadanda lamarin ya rutsa da su suna cikin motar cocin ne suna tafiya domin halartan wani taro lokacin da aka kai musu harin.
Legit.ng ta tattaro cewa wani mai amfani da Facebook, Eje Kenny Faraday, ya sanar da labarin a shafinsa tare da hoton farar motar a yammacin ranar Juma’a, 26 ga Maris.
Ya rubuta cewa:
“Dukkan fasinjojin da ke cikin wannan motar an yi garkuwa da su ne a kan titin Kachia, kilomita 63 daga Kaduna.”
Jaridar ta kuma lura da cewa wata majiya ingantacciya da kuma wani jami’in cocin, wanda suka yi magana bisa sharadi sakaya sunansu, sun tabbatar da rahoton.
An ruwaito majiyar ta ce: “Su takwas ne a cikin bas din. Za su je Kachia a shirye-shiryen cocin na bikin Ista. ‘Yan bindigar sun fitar da su daga motar bas din sannan suka sanya su a cikin motarsu na aiki. Har yanzu ba su tuntubi cocin ba. ”
A cewar rahoton, jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar, Mohammed Jalige, ya ce yana ci gaba da bincike kan lamarin.
Jami’an hukumar yaki da masu almundahar kudi ta EFCC ta kama Ibeh Theophilus Uche, Shugaban 10 Kobo Wine Place da ke Ikotun a Legas tare da mahaifiyarsa kan zarginsa da […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)