play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Shugaba Buhari zaiyi jawabi kan matsalar tsaro

Tsaro

Shugaba Buhari zaiyi jawabi kan matsalar tsaro

Bello Sani December 9, 2020


Background
share close

Shugaban kasa kasar Najeriya Muhammadu Buhari zai hallara gaban zaman majalisun dokokin tarayyar kasar a jibi Alhamis domin yin jawabi kan batun harkokin tsaro.

Hakan na cikin wani jawabi da mai taimaka wa shugaban kasa Muhammdu Buhari kan kafofin sada zumunta, Lauretta Onochie ta wallafa a shafinta na Twitter.

Ana tunanin jabawabin shugaban zai mayar da hankali kan matsalar tsaro da ke damun arewacin kasar.

A makon da ya gabata mayakan Boko Haram suka kashe Manoma arba’in da uku a Zabarmari jihar Borno tare da yanka wasu bakwai a jihar Katsina da tafiya sama da talatin, wanda haka ya sanya majalisar wakilai ta gayyaci shugaban don ya hallara a gabanta wanda kuma ya amsa goron gayyatar.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *