play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Sarauta
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Sarkin Kano Ya Dakatar Da Mai Unguwar Sabon Gari Bisa Zargin Sa Da Siyar Da Jaririya

Sarauta

Sarkin Kano Ya Dakatar Da Mai Unguwar Sabon Gari Bisa Zargin Sa Da Siyar Da Jaririya

Bello Sani August 26, 2020 14


Background
share close

Masarautar Kano ta dakatar da Mai Unguwar Sabon Gari, Ya’u Muhammad bisa zargin sa da hannu wajen siyar da wata jaririya.

Muhammad Umar, Sakataren Galadiman Kano, Abbas Sunusi ne ya bayyana wannan dakatarwa ranar Talata a Kano, kamar yadda jaridar Intanet, Kano Focus ta rawaito.

Mista Umar ya ce Majalisar Masarautar Kano ta dakatar da Mista Muhammad har zuwa lokacin da Hukumar Hana Fataucin Bil’adama ta Ƙasa, NAPTIP za ta kammala bincike.

NAPTIP tana bincikar Mista Muhammad tare da Kwamandan Hisbah na Fage, Jamilu Yusuf bisa zargin su da siyar da jaririya ga wata ‘yar ƙabilar Ibo a kan kuɗi N20,000

Duka mutanen biyu sun musanta zargin.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *