play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Nan da wani ɗan lokaci za a buɗe iyakokin ƙasar nan – Zainab Ahmed

Siyasa

Nan da wani ɗan lokaci za a buɗe iyakokin ƙasar nan – Zainab Ahmed

Bello Sani November 25, 2020 9


Background
share close

Ministar Kuɗi ta ƙasa Zainab Shamsuna Ahmed, ta ce za a iya buɗe kan iyakokin ƙasar nan ba da jimawa ba.

Zainab Shamsuna Ahmed ta bayyana hakan ne a lokacin da ta ke zantawa da manema labarai na fadar gwamnatin tarayya a yau Laraba, ta ce kwamitin fadar shugaban ƙasa da aka kafa kan lamarin ya kammala aikinsa kuma ya bayar da shawarar a buɗe.

Ta ƙara da cewa nan ba da ɗaɗewa ba kwamitin zai gabatar da rahotonsa ga shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, daga nan kuma za a gabatar da sanarwa a hukumance kan lamarin.

A cikin watan Agustan shekarar 2019 ne gwamnatin tarayya ta rufe iyakokin ƙasar nan da zummar daƙile yawaitar fasa-kwauri da kuma bunƙasa tattalin arziki.

Matakin rufe iyakokin ya ja hankalin mutane da dama a kasar nan tare da jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu ke goyon baya wasu kuma ba sa goyon baya.

A cikin watan Maris din shekarar da mu ke ciki fadar shugaban ƙasa ta ce ‘yan kasar nan sun ga irin amfanin da rufe iyakokin ya yi a fannin tattalin arzikinta.

Malam Garba Shehu, kakakin Shugaba Muhammadu Buhari, wanda shi ne ya bayyana hakan, ya jaddada cewa ba za a bude iyakokin kasar ba sai gwamnati ta samu tabbaci daga wurin makwabtanta cewa ba za a su rika yin abubuwan da suka saba wa doka ba a kan iyakokin.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *