play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Zamantakewa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Na Bar Mijina Saboda Girman Mazakutarsa, Matar Aure ta Shaidawa Kotu

Zamantakewa

Na Bar Mijina Saboda Girman Mazakutarsa, Matar Aure ta Shaidawa Kotu

Bello Sani March 27, 2021 24


Background
share close

An kama wata mata yar kasar Kenya mai suna Lucy Njeri an gurfanar da ita a gaban kotu da ke Makadara kan tsohon mijinta wanda a yanzu ta ce auren ya mutu, rahoton Vanguard.

A cewar hujjar da mai karar ta gabatar a kotu, ta yi ikirarin cewa ta dade da cire tsammani kan mijinta domin duk lokacin da ya kusance ta, mazakutarsa na yi mata rauni domin ya yi girma da yawa.

Ta ce daga bisani ta gaji, ta kwashe kayanta ta bar gidasa, ta shaida masa cewa ba za ta dawo ba amma ya cigaba da zuwa gidanta yana domin duba ta duk da barazanar da ta ke masa na cewa ya dena zuwa.

An gano cewa a daren da ta watsa tsohon mijinta, Geoffrey Nyebere, acid, ya tafi gidan misalin karfe 10 na dare a ranar 16 ga watan Janairun 2021 ya fara kwankwasa kofa.

Lucy ta ce tana kan gado tare da saurayinta kuma ta ki bude masa kofa ta umurci ya fice ya bar mata harabar gida amma bai yi hakan ba ya cigaba da kwankwasa kofar, don haka sai ta bude kofa ta watsa masa acid a kirki, ta lalata masa fuska.

Da mutane suka fara taruwa yayin da mutumin ke cikin azaba, matar da saurayinta sun tsere amma an kama su bayan kwana daya.

Shi kuma tsohon mijin an garzaya da shi asibiti don masa magani.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *