play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Mutane da dama sun jikkata sakamakon fashewar tunkunyar gas a Legas

Labarai

Mutane da dama sun jikkata sakamakon fashewar tunkunyar gas a Legas

Bello Sani April 13, 2021 3


Background
share close

An samu fashewar gas a karamar hukumar Amuwo-Odofin na jihar Legas a ranar Talata 12 ga watan Afrilun shekarar 2021, The Punch ta ruwaito.

An gano cewa mutane da dama sun jikkata sakamakon lamarin da ya faru a layin Iyasoko da ke Agboju, Amuwo-Odofin.

An ruwaito cewa lamarin ya faru ne misalin karfe 6.55 na yamma.

Mai magana da yawun hukumar bada agajin gaggawa na Legas, LASEMA, Nosa Okunbor ya tabbatar da fashewar gas din inda ya ce an tura jami’ai masu ceto zuwa wurin misalin karfe 6.50 na yamma.

Ba a tantance adadin mutanen da goborar ta shafa ba a lokacin hada wannan rahoton.

Ya ce, “Eh, da gaske ne. Tawagar jami’an mu suna hanyarsu na zuwa wurin. Cinkoson ababen hawa ne ya sa suka yi jinkiri. Ba zan iya tantance irin barnar da ta faru ba a yanzu.”

 

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *