play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Mata 30 Dake Tsare a Kasar Lebanon Sun Nemi Gwamnati ta Dawo Dasu Najeriya

Tsaro

Mata 30 Dake Tsare a Kasar Lebanon Sun Nemi Gwamnati ta Dawo Dasu Najeriya

Bello Sani August 1, 2020 5


Background
share close

Wasu mata guda 30 yan Najeriya da aka shigar dasu kasar Lebanon ta barauniyar hanya sunyi kira ga gwamnatin Najeriya da ta dawo dasu kasarsu ta gado sakamakon matsanancin halin rayuwa da suka tsinci kansu aciki.

Wannan bayanin ya fito daga bakin shugaban gamayyar yan jarida masu kula da sufuri tsakanin kasa da kasa Ajibola Abayomi. Inda yayi kira ga gwamnati wajan gaggauta yin bincike tare da hukunta duk wanda aka samu da laifi.

Shugaban yace an ajiye matan ne su 30 a daki guda mai bandaki mara kyau a garin Dawra dake kasar Lebanon. Daga cikin matan akwai wanda ta fito daga jihar Ondo inda take cewa sun gudo ne daga gidan da suke aiki soboda cin zarafinsu da akeyi ta hanyar yi musu kwacen kayansu, tsefe musu gashi da yi musu aski da reza da kuma hanasu kudinsu na aiki da sukayi.

Tuni hukumomi masu yaki da fataucin bayi na kasashen duniya suka fara bada gudunmawarsu wajan tabbatar da cewa an taimaka wa wadannan mata guda 30 tare da hukunta duk wanda aka samu da laifi.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *