
Da mu rasa Karnukanmu gara iyayenmu Mata su mutu inji Mafarauta a Kano
Wani mafarauci mai suna Ado Muhammad Maiduna ya bayyana cewa da yawa mafarauta da su rasa karnukansu gara a ce sun rasa uwar da ta haife su. Ado Muhammad Maiduna […]
Gaba Tsakanin Makota Bello Sani
Tun bayan bullar cutar coronovirus gwamnatin jihar Kano ta dauki matakin garkame makarantun boko da na Allo dama islamiyyu da kuma gidajen kwallon kafa dama gidajen da ake gudanar da bukukuwa da kuma kasuwannin jihar Kano, da nufin kare kai daga cutar ta Coronavirus.
Amma bayan daukar wasu tsawan lokuta a hankali-a hankali za’a iya cewar an bude gurare da yawa amma banda makarantun islamiyyu dana boko.
Haka kuma a baya – bayan nan gwamnati ta bude wasu makarantun bokon da nufin daliban ajin ƙarshe su rubuta jarrabawar WAEC da NECO.
Kusan za’a iya cewa wannan dalili ne ya sa wasu malaman islamiyyu bude makarantun su, amma sai gashi ta gwamnati ta yi umarni da su rufe ko su fuskanci hukunci.
Wasu malaman islamiyyu a yankin karamar hukumar Tarauni a jihar Kano, sun bayyana cewa ya kamata gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya duba wannan al’amari, la’akari da yan da ake masa lakabi da Khadimul Islama ya waiwayi makarantun Islamiyyu domin suna cikin wani hal.
Wani malamin Islamiyya wanda ya bukaci a sakaye sunansa ya ce daga yau sun sauke gwamna Abdullahi Umar Ganduje daga matsayin Khadimul Islama, domin har yanzu ya ki yin wata hobbasa domin bude makarantun Islamiyyu a fadin jihar Kano.
Tuntuni dai gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayar da umarnin bude gidajen kallon kwallon kafa da gidajen bukukuwa amma kuma har yanzu Islamiyyu sun gagara budewa
Wani mafarauci mai suna Ado Muhammad Maiduna ya bayyana cewa da yawa mafarauta da su rasa karnukansu gara a ce sun rasa uwar da ta haife su. Ado Muhammad Maiduna […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)