play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Kiwon Lafiya
  • keyboard_arrow_right Lokacin dokar kullen korona zagaye na biyu ya ƙarato

Labarai

Lokacin dokar kullen korona zagaye na biyu ya ƙarato

Bello Sani November 13, 2020 7


Background
share close

Ƙungiyar jami’an kiwon lafiya da ke binciken cutuka ta ƙasa wato ARIN, ta ce rakuni na biyu na kullen COVID-19 ya kusanto saboda ƙaruwar yawan masu kamuwa da cutar korona a cikin makonnin da su ka gabata.

Shugaban reshen ƙungiyar na birnin tarayya Abuja Dokta Ohikhoakhai Wellington, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja.

Ohikhoakhai Wellington, ya ce tuni masana da masu sharhi akan al’amuran yau da kullum su ka bayyana shekarar 2020 a matsayin shekarar annoba sakamakon cutar corona da illolin da take haifarwa a tsakanin al’ummomi da tattalin arziki.

Wannan dai yana zuwa a daidai lokacin da hukumar dakile ya duwar cututtuka ta ƙasa NCDC ta fitar da sanarwar samun karin mutum 180 a suka harbu da cutar Coronavirus a faɗin ƙasar nan.

A sakon da hukumar ta fitar a daran jiya ya nuna cewa adadin mutum 64,516 ne a ka tabbatar da sun kamu da cutar ta korona.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *