play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Ilimi
  • keyboard_arrow_right Kyakkyawar ‘yar Arewa ta kammala jami’a, yan Najeriya sunce kyanta kadai na iya rikitar da Alkali

Labarai

Kyakkyawar ‘yar Arewa ta kammala jami’a, yan Najeriya sunce kyanta kadai na iya rikitar da Alkali

Bello Sani February 16, 2021 6


Background
share close

Yan Najeriya sun kwararawa wata budurwa sakonnin taya murna ga kyakkyawar budurwa yar Arewa bisa nasaran da ta samu.

Budurwar mai suna Maryam Musa ta yi sanarwa a shafin Tuwita bisa kammala karatun digirinta a fannin karatun lauya.

Maryam, wacce bata bayyana jami’ar da ta kammala ba ta godewa Allah bisa nasarar da ta samu.

Yan Najeriya sun jinjina mata bisa irin kyawun da Allah ya bata yayinda wasu ke taya ta murnan kammala karatunta.

Hakazalika wasu sun bata shawari kan rayuwa bayan karatu.

Wasu daga cikin mabiyanta a twitter sun bayyana ra,ayinsu kamar haka:
@AliyuIbrahimA13 yace: “Ina tayaki murna Barista. ina bukatar kyakkyawar lauya irinki, wacce za ta iya rikita Alkali.”

@Mushin24789 yace; “Ki kasance mai gaskiya duk inda kika samu kanki kuma kada kiyi rashin adalci a aiki…”

@Omacares1 yace: “Allah ya cigaba da kare ki da shiryar dake hanya madaidaici bisa wannan babban nasara.”

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *