A ranar Laraba, 3 ga watan Maris, 2021, kungiyar kabilar Ibo, Ohanaeze Ndigbo, ta ce hana shigo da abinci da wasu kungiyoyin Arewa su kayi ba zai taba su ba.
Jaridar Punch ta ce Ohanaeze Ndigbo ta tuna yadda aka yi yakin basasa na Biyafara, inda yankin kasar su ka shafe watanni kusan 30 ba tare da sun samu abinci ba.
Wannan kungiya ta yi magana ne ta bakin mai magana da yawunta, Cif Alex Ogbonnia, wanda ya ce kin kawo masu kayan abinci daga Arewa ba wani abin kuka ba ne.
“A wani bangare, su ne ke zaluntarmu. Su ke auka mana. Arewa ta dade ta na jawo matsaloli ta hanyoyi iri-iri. Da mamaki a ce sun fara zanga-zanga, su na bore.”
Hako ma’adanai da ake yi a Zamfara ya na cikin dalilan rashin zaman lafiya Shakka babu akwai arzikin ma’adanai a Najeriya, a 2017 akwai sama da mutane 600, 000 da […]
Post comments (0)