play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right KAROTA za ta tarawa jihar Kano fiye da naira biliyan ɗaya

Siyasa

KAROTA za ta tarawa jihar Kano fiye da naira biliyan ɗaya

Bello Sani November 10, 2020 6


Background
share close

Shugaban hukumar da ke kula da zirga-zirgar ababen hawa a jihar wato KAROTA, Dakta Baffa Babba Dan’agundi ya bayyana cewa hukumar ta sa za ta tarawa jihar Kano haraji na naira biliyan Ɗaya da miliyan 500 a cikin shekara mai kamawa ta 2021.

Dakta Bappa Babba Ɗan-Agundi ya bayyana haka ne a lokacin da yake kare kasafin kuɗin hukumar a zauren Majalisar Dokokin Jihar Kano a yau Litinin.

Shugaban KAROTAR ya ƙara da cewa Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya baiwa hukumar damar ɗaukar sabbin ma’aikata har 1,400.

Ya ce a halin da ake ciki, hukumar KAROTA ta ɗauki ma’aikata 700, zuwa Janairu, 2021 kuma za su ƙara ɗaukar wasu sabbin ma’aikatan 700.

A ƙarshe shugaban na KAROTA ya ce hukumarsa za ta haɗa kai da Hukumar Gyara Tituna ta Jihar Kano, KARMA, domin ganin sun tsaftace jihar.

 

Kakaki24

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *