
KO KUSAN AMSAR TAMBAYAR BARIN TAKUNKUMI A FUSKA YANADA ILLA KO HALAKA MUTUM?
A shafukan sada zumunta, ana ci gaba da yaɗa wani saƙo da ke bayyana cewa akwai hatsari a sanya takunkumin fuska mai ba da kariya daga ɗaukar cutar korona. Sakon, […]
Gaba Tsakanin Makota Bello Sani
Rundunar ‘yan sanda a Adamawa, a ranar Lahadi, ta tabbatar da mutuwar wani da ake zargi da zama mamba a wata kungiyar gungun masu laifi da aka fi sani da‘ Shila Boys’ a Jimeta, karamar hukumar Yola ta Arewa.
Wasu ‘yan zanga-zanga sun kona dan kungiyar Shila har lahira bisa zargin cewa ya yi wa wata mata sata da kuma daba mata wuka, Daily Trust ta ruwaito.
Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar, DSP, Sulaiman Nguroje, ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a ranar Lahadi a Yola.
– Wasu fusatattun jama’ar gari sun afkawa wani da ake zargi da aikata fashi da makami a Yola
– Mutanen sun samu nasarar cinna wa dan fashin wuta kuma ya kone kurmus har lahira
– Rundunar ‘yan sandan Adamawa ta tabbatar da farruwar haka, kuma sun dauki gawar wanda aka kashen
Rundunar ‘yan sanda a Adamawa, a ranar Lahadi, ta tabbatar da mutuwar wani da ake zargi da zama mamba a wata kungiyar gungun masu laifi da aka fi sani da‘ Shila Boys’ a Jimeta, karamar hukumar Yola ta Arewa.
Wasu ‘yan zanga-zanga sun kona dan kungiyar Shila har lahira bisa zargin cewa ya yi wa wata mata sata da kuma daba mata wuka, Daily Trust ta ruwaito.
Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar, DSP, Sulaiman Nguroje, ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a ranar Lahadi a Yola.
Nguroje ya ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar da misalin karfe 7:00 na dare.
Ya ce an dauki gawar wanda ake zargin ne daga rundunar Jimeta da ke Jimeta.
Ya fadawa NAN cewa mambobin kungiyar su uku, suna kan keke ne yayin da suka yi wa matar fashin a hanyar Mubi da ke Jimeta.
“Matar (an sakaya sunanta) ta yi ihu don neman taimako kuma nan take, wasu fusatattun mutane suka bi wadanda ake zargin, suka kama daya daga cikinsu suka cinna masa wuta.
“Sauran ‘yan kungiyar biyu kuwa, sun tsere,’’ Nguroje ya fada wa NAN.
A shafukan sada zumunta, ana ci gaba da yaɗa wani saƙo da ke bayyana cewa akwai hatsari a sanya takunkumin fuska mai ba da kariya daga ɗaukar cutar korona. Sakon, […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)