play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Ina da ƙwarin gwiwar Mace na iya gadon Buhari

Siyasa

Ina da ƙwarin gwiwar Mace na iya gadon Buhari

Bello Sani November 11, 2020 11


Background
share close

Mataimakiyar Sakare Janar na Majlisar Dinkin Duniya, Amina J Mohammed,ta kalubalanci matan ƙasar nan kan su kara jajircewa wajen ganin sun karbi ragamar shugabancin Najeriya idan shugaba Muhammadu Buhari ya kammala wa’adinsa a 2023.

Amina wacce ke jagorantar manyan jami’an majalisar da ke wata ziyarar aiki a Najeriya ta bayyana hakan ne a ranar Talata a Abuja.

Tun da farko dai sai da tawagar ta gana da shugaba Buhari a fadar sa ta Aso Rock inda suka tattauna a kan hanyoyin sake gina kasar bayan mummunar illar da annobar COVID-19 ta yi mata.

Amina, wacce tsohuwar Ministar Muhalli ce a Najeriya ta ce dole ‘yan Najeriya su tashi tsaye wajen gina kasa ba tare da la’akari da banbance-banbancensu na siyasa ba.

Ta ce, “Ya kamata mu fahimci abinda yake daidai domin muga ya faru, a rukuninmu ko a daidaikunmu. Akwai bukatar girmama kowanne bangare na kasarmu saboda kowa na da irin gudunmawar da zai bayar wajen gina kasa.”

Da aka tambayeta ko tana da sha’awar tsayawa shugabancin idan Buharin ya kammala mulki sai ta ce, “Wannan sh ine fata na, bana tunanin mace ba za ta iya ba. Na yi amannar cewa duk wanda ya yi kokari zai iya cimma burinsa.

“Saboda haka dole mata su tashi tsaye. Suna da kusan kaso 50 cikin 100 na kuri’un da ake kadawa, idan har za su iya neman goyon bayan maza, me zai hana su cimma burinsu? Ban ga dalilin da zai sa ace mace ba za ta mulki Najeriya ba.

A cikin watan Disambar shekarar 2016 ne Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya nada Amina Mohammed a matsayin mataimakiyarsa.

 

Kakaki24

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *