play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Ilimin Ƴaƴa Mata: Gwamnatin Kano za ta ɗauki malamai 2000 domin karantar da ƴan mata

Siyasa

Ilimin Ƴaƴa Mata: Gwamnatin Kano za ta ɗauki malamai 2000 domin karantar da ƴan mata

Bello Sani November 25, 2020 19


Background
share close

Gwamnatin jihar Kano ta ce, ta fara shirye-shiryen daukar malamai guda 2000 domin aikin karantar da dalibai a makarantun ’yan mata da ke fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Malam Sanusi Kiru ne ya bayyana kudirin gwamnatin na daukar malamai dubu biyu yayin da yake jawabi a wurin taron kaddamar da wata gidauniyar tallafawa ’ya’ya mata (AGILE).

A cewar Kwamishinan, manufar shirin daukar malaman shi ne cike gibin da ake da shi tare da bunkasa harkokin ilimi musamman na yara mata a jihar.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ruwaito Kwamishinan yana cewa wannan shiri na hadin gwiwa ne tare da wasu jihohi bakwai da Gwamnatin Tarayya da kuma Asusun Bankin Duniya.

Jihohin sun hada da: Kano da Kaduna da Katsina da Kebbi da Filato da Ekiti da kuma Borno.

Sanusi Kiru ya ce, tuni gwamnatin jihar Kano ta fara gina kanana da manyan makarantun sakandire guda 120 a fadin jihar tare da tanadar motocin bas-bas da za su rika zirga-zirgar daukar dalibai mata ’yan makaranta a kwaryar birnin jihar.

Ya kuma ce Gwamnati ta biya wa dalibai mata kimanin 489 kudin jarabawar kammala babbar sakandire ta NECO, da kuma ware naira biliyan 4 don ciyar da dalibai mata ’yan makarantun kwana a fadin jihar.

Kwamishinan ya kara da ce wa, bunkasa ilimin yara mata na daga cikin manufofin gwamnatin Dokta Abdullahi Umar Ganduje wanda ya ce yana ci gaba da aiki tukuru ba dare ba rana don ganin an inganta ilimin yara mata a jihar.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *