play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right Harin Jangebe: Ganduje ya bada umurnin rufe makarantun kwana 10 a Kano

Labarai

Harin Jangebe: Ganduje ya bada umurnin rufe makarantun kwana 10 a Kano

Bello Sani February 27, 2021 11


Background
share close

Gwamnatin jihar Kano ta bada umurnin rufe makarantun kwana guda 10 a sassan jihar

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da rufe makarantun kwana 10 a sassan jihar nan take biyo bayan sace yan matan makarantar GGSS Jangebe a jihar Zamfara, Daily Trust ta ruwaito.

Kwamishinan Ilimi na jihar, Muhammad Kiru ya ce gwamnatin ta cimma matsayin ne bayan nazari da bita kan abubuwan da ke faruwa a jihohin da ke makawabtaka da ita inda ake sace dalibai.

cewarsa, rashin tsaron ne ya tilastawa gwamnatin daukar matakin domin kare lafiya yaran.
Ya ce iyaye da masu kulawa da yara su tafi su kwashe yaransu daga makarantun, nan gaba gwamnati za ta sanar da ranar da za a bude makarantun don cigaba da karatu.

Ya lissafa makarantun da abin ya shafa kamar haka: Maitama Sule Science College, Gaya; Boarding Secondary School, Ajingi; Girls Secondary Schools a Sumaila, Gezawa da Jogana, Kachako da wani a Unguwar Gyartai a Kunchi da kuma Girls Secondary School, Albasu,
Sauran sun hada da Makarantar Sakandare ta maza da ke Maiyaki da Unity College a Karaye.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *