play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Kiwon Lafiya
  • keyboard_arrow_right Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗi kan riga-kafin korona na jabu

Labarai

Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗi kan riga-kafin korona na jabu

Bello Sani January 16, 2021 8


Background
share close

Hukumomin Najeriya sun yi gargaɗi kan wani riga-kafin korona na jabu dake yawo a faɗin ƙasar.

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna NAFDAC ta ce ba ta amince da ko wane riga-kafi ba.

Shugabar hukumar Mojisola Adeyeye ta bayyana cewa ta tashi tsaye haiƙan wajen hana shigar riga-kafin na jabu hannun jama’a ba.

A baya-bayannan hukumomi sun ce suna fatan yi wa kaso 40 cikin ɗari na ƴan kasar riga-kafin a 2021.

Yayin da ake fuskantar ƙaruwar masu kamuwa da cutar ta korona, akwai fargabar cewa wasu miyagu ko ƙungiyoyi za su iya amfani da halin da ake ciki su samar da riga-kafin da ba a amince da shi ba a kasuwannin bayan fage.

A ranar Alhamis cutar ta kashe mutum 23 a Najeriya, wanda shi ne mafi yawa tun bayan da korona ta ɓulla a Najeriya, kuma adadin waɗanda suka kamu ya kai 105,478 a cikin wata goma sha ɗaya.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *