play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Gwamnatin Kano ta karyata batun rusa makarantar Sheikh Abduljabbar Kabara

Siyasa

Gwamnatin Kano ta karyata batun rusa makarantar Sheikh Abduljabbar Kabara

Bello Sani February 7, 2021 4


Background
share close

Gwamnatin jihar Kano ta karyata batun rushe ginin makarantar Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara da ke birnin jihar.

Kakakin hukumar tsara muhalli ta jihar Kano wato KANUPDA, Ado Muhammad Gama, ya sanar da sashin Hausa na BBC cewa gine-ginen da aka rusa suna kusa da wajen da malamin ke bayar da karatu amma ba nasa ba ne,
Ya ce:

“Su gine-ginen da ake magana a kai, wasu mutane ne suka yi su ba bisa ka’ida ba shi ya sa yanzu muka rusa su.

Tunda farko dai An bukaci mutanen da suka yi ginin a kan kada su soma shi amma sai suka yi burus da batun shi ya sa aka rusa fine ginen masu.

Ya kuma tabbatar da cewar makarantar Sheikh Abduljabbar tana nan babu abin da ya same ta.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *