play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Gwamnan Borno Ya Caccaki Sojojin Jihar

Siyasa

Gwamnan Borno Ya Caccaki Sojojin Jihar

Bello Sani July 31, 2020 85


Background
share close

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya caccaki sojoji bisa harin da aka kaiwa tawagar sa a garin Baga na Karamar hukumar Kukuwa.

Gwamna Zulum dai ya bar Birnin Maiduguri ne a yammacin ranar Litinin zuwa arewacin jihar domin cigaba da rabon kayan abinci wanda ya fara tun farkon watan Yuli.

A ranar Laraba ya tsara zuwa garin Baga garin dake kusa da tafkin Chadi wanda ya taya da kayar baya suke rike da shi a shekarun baya har sai da jami’an tsaro suka kwace garin.

Sai dai tazarar kila mita kadan da garin yan bindiga suka bude wuta kan tawagar Gwamnan. Sai dai jami’an tsaron dake tsare da lafiyar gwamnan sun mayar da martani ga maharan.

Zulum wanda yake cikin fushi ya caccaki jami’in sojan dake kula da yankin Mile 4 bisa gazawar sojojin wajen hana yan ta’adda mamayr garin Baga.

“Kun kasance anan tsawon shekara guda , akwai sojoji 1,181 anan, idan baza ku iya kare garin Baga ba wanda yake kasa da kilomita biyar daga sansanin ku toh ya kamata mu manta da Baga. Zan fadawa babban hafsan soja na kasa ya kawo mazaje a sauran gurare da zasu yi amfani. Inji Zulum.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *