play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right Daliban Jangebe sun ce da maigadinsu aka hada kai wurin sacesu, Matawalle

Labarai

Daliban Jangebe sun ce da maigadinsu aka hada kai wurin sacesu, Matawalle

Bello Sani March 4, 2021 13


Background
share close

Gwamnan Zamfara ya sanar da cewa maigadin makarantar Jangebe yana daya daga cikin wadanda aka hada kai dasu wurin sace yaran

Bello Matawalle, gwamnan jihar Zamfara ya ce ‘yammatan Jangebe sun bayyana cewa maigadinsu na makaranta yana daga cikin wadanda aka hada kai dasu aka sacesu.

A ranar Laraba da ta gabata ne Matawalle ya bayyana a shirin siyasarmu a yau na gidan Talabijin na Channels.

Sama da dalibai 270 ne aka sace a makarantar gwamnati da ke garin jangebe na karamar hukumar Talata-Mafara da ke Zamfara a watan Fabrairu. An sako su a ranar Talata.

A yayin da aka bukaci ya bayyana wadanda suka sace yaran, gwamnan yace ‘yan bindigan sun sanar da cewa har da maigadin suka hada baki.

Matawalle yace ana bincike a kan haka amma bai sanar da sauran wadanda aka hada kai dasu ba.

“Har da maigadin makarantar. Yaran sun sanar da hakan kuma sun ce bayan an sakesu, ‘yan bindigan sun ce su gaishe musu da maigadin makarantarsu,” yace.

“Sun kara da bayyana sunansa a matsayin wanda ya ce su zo a lokacin su kwashe yaran, don haka da hannunsa a ciki.

“Sun sanar da hakan a gaban kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, za a yi bincike a kan hakan sannan a gano dukkan wadanda ke da hannu a ciki.”

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *