play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Tattalin Arziki
  • keyboard_arrow_right Babu kudi a Najeriya, sai da aka buga sabbin kudi N60bn aka raba mana a watan Maris, Gwamna Obaseki

Labarai

Babu kudi a Najeriya, sai da aka buga sabbin kudi N60bn aka raba mana a watan Maris, Gwamna Obaseki

Bello Sani April 11, 2021 29


Background
share close

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya bayyana cewa Najeriya na cikin halin rashin kudi saboda sai da aka buga wasu biliyoyi a watan Maris aka rabawa jihohi.

Gwamnan ya ce kudin wata-wata da ake rabawa gwamnoni bai kai ba, sai da gwamnatin tarayya ta buga sabbin kudi bilyan 50 zuwa 60 aka raba musu.

“Lokacin da aka biyamu kudin wata-wata na Maris, sai da gwamnatin tarayya ta buga N50-N60 billion don kudin su isa a raba mana,” Obaseki ya bayyana ranar Alhamis.

“A wannan watan na Afrilu, zamu sake komawa Abuja a raba mana kudi. A karshen shekarar nan adadin bashin da muka ci zai zama tsakanin N15-N16 trillion.”

Kawai karban bashin kudi akeyi babu hanyar biya, amma hankalin kowa na kan 2023, kowa na ganin laifin shugaban kasa sai kace boka ne.”

“Najeriya ta canza. Tattalin arzikin Najeriya ya canza gaba daya tun bayan yakin basasa, kawai kame-kame mukeyi.”

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *