play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right An sace yara shida ‘yan gida daya a Zamfara

Labarai

An sace yara shida ‘yan gida daya a Zamfara

Bello Sani January 9, 2021 7


Background
share close

Rundunar ‘yan sanda a jihar Zamfara ta tabbatar da sace yara shida, ‘ya’ya ga Alhaji Sani Gyare da ke kauyen Kadauri a karamar hukumar Maru.

Kakakin rundunar, SP Shehu Muhammed ne ya tabbatarwa da kamfanin dillacin labaran Najeriya – NAN a birnin Gusau.

A cewarsa, ‘yan sanda sun samu labarin sace yara bakwai, shida a gidan Alhaji Gyare sai kuma yarinya ta bakwai a gidan wani makwabcinsa duk a kauyen Kadauri.

“Kwamishinan ‘yan sanda, CP Abutu Yaro ya tura runduna ta musamman domin ceto yaran,” in ji kakakin ‘yan sandan.

Bayanai sun nuna cewa masu garkuwa da mutane sun isa kauyen ne a ranar Juma’a da daddare inda suka aikata wannan mummunan aikin.

Sace mutane domin karbar kudin fasa na kara yawaita a jihohin arewa maso yammacin Najeriya musamman jihohin Katsina, Zamfara da Kaduna.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *