play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Addini
  • keyboard_arrow_right An fara bincikar jami’in Hisbah da aka kama da matar aure a ɗakin Otel a Kano

Labarai

An fara bincikar jami’in Hisbah da aka kama da matar aure a ɗakin Otel a Kano

Bello Sani February 17, 2021 6


Background
share close

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ce ta kafa kwamiti na bincike kan wani jami’in ta da ake zargi da kwartanci da matar aure

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kafa kwamiti mai mutum biyar domin fara bincike kan jami’inta, Sani Rimo, wanda aka ce an kama shi da matar aure a cikin dakin Otel a Kano.

Babban Kwamandan Hisbah, Harun Ibn-Sina, ya tabbatar da cewa an bawa kwamitin wa’adin kwanaki uku ta yi bincike kan lamarin, Daily Nigerian ta ruwaito.

Na kafa kwamitin bincike na kuma na bata wa’adin kwanaki 3 domin ta bata rahoton ta. Na kuma gayyaci bangarorin da abin ya shafa domin su bada ba’asi

“Hisbah tana da dokokin ta, kuma idan muka same shi da laifi, za mu dauki matakin da ya dace a kansa bisa yadda dakokin mu suka tanada,” in ji shi.

Rahotanni sun ce dan sanda daga ofishin Noman’s Land ne ya kama Mista Rimo a dakin wani otel a yankin Sabon Gari da ke Kano.

Majiyoyi daga rundunar yan sanda sun ce sun samu rahotanni ne game da shi sannan suka garzaya suka kama shi tare da matar a dakin.

A baya Mista Rimo shine jami’in tawagar yaki da masu karuwanci na hukumar ta Hisbah wanda karuwai ke shakkarsa sosai a yankin na sabon gari.

A halin yanzu shine jami’in da ke kula da sashin masu hana bara a Kano.

Kawo yanzu yan sanda ba su yi martani kan lamarin ba.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *