play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Shariah
  • keyboard_arrow_right Alkali ya dakatar da NCC, Pantami daga garkame layukan waya saboda rashin NIN

Labarai

Alkali ya dakatar da NCC, Pantami daga garkame layukan waya saboda rashin NIN

Bello Sani March 31, 2021 46


Background
share close

Jaridar Punch ta ce babban kotun tarayya da ke Legas ya hana gwamnatin tarayya toshe layukan wayoyi watau SIM da ba ayi masu rajistar lambar NIN ba.

Ma’aikatar sadarwa da tattalin arzikin zamani ta bada umarni ta hannun hukumar NCC, ta bukaci kamfanoni su rufe duk wani layin wayar da bai da lambar NIN.

Wannan mataki da NCC ta dauka ya sa tsohon mataimakin shugaban kungiyar NBA na kasa, Monday Ubani, ya kai kara kotu, ya na kalubalantar gwamnati.

Babban lauya Monday Ubani ya nemi a hana NCC toshe layukan da ba a hada su da lambar ta NIN ba.

A karshe Alkali M.A Onyetenu ya yanke hukunci cewa a tsawaita wa’adin da watanni biyu daga ranar da aka zartar da hukunci, ya ce wa’adin da aka sa ya kure.

Mai shari’a Onyetenu ya karbi kukan lauyan, ya ce kokarin yin rajistar NIN cikin wahala, zai ci karo da sashe na 39 da 41 na tsarin mulki a kan damar ‘yan kasa.

Alkalin ya kuma ce tursasa wa mutane har miliyan 200 yin rajistar lambar NIN ta ‘yan kasa a lokacin da ake fama da annobar COVID-19, zai jefa jama’a cikin hadari.

Kwanaki kun ji yadda Hukumar sadarwan Najeriya, watau NCC ta umurci dukkannin kamfanonin sadarwa su dakatar da rijistar sababbin layukan waya.

NCC ta bada wannan umurnin ne saboda manufar gwamnatin tarayya na duba rumbun wadanda su kayi rajista da kuma tabbatar da cewa kamfanonin na bin dokoki.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *