
Gaba Tsakanin Makota Bello Sani
Bello Sani November 22, 2020 7
Najeriya ta fada cikin matsin tatalin arziki a karo na biyu cikin shekaru 5 sakamakon annobar Covid 19 da faduwar farashin danyen mai, kamar yadda hukumar kididdiga ta kasar nan ta bayyana a jiya Asabar.
Kudaden shigar da kasar nan ta ke samu a cikin rubu’i na 3 na wannan shekarar ya yi kasa a karo na 2 a jere, da kashi 3 da digo 62, a cewar hukumar kididdiga ta NBS.
Hukumar ta NBS ta dora alhakin haka a kan faduwar farashin danyen mai a kasuwannin duniya da kuma tasirin annobar coronavirus.
Kudaden shiga da ke da nasaba da danyen mai ya yi kasa da kusan kashi 14, idan aka kwatanta da kusan kashi 7 a rubu’i na 2, a cewar hukumar.
Asusun ba da lamuni na duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin kasar nan zai rikito da sama da kashi 5 a wannan shekarar, amma gwamnatin tarayya ta ce zai fadi da kusan kashi 9.
Najeriya, wacce ita ta fi samar da danyen mai a nahiyar Afrika, kafin yanzu, tana samar da ganga miliyan 2 ne duk rana, amma tasirin annobar covid 19 ya sa ta sauka zuwa ganga miliyan 1 da dubu dari 4.
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)