play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Siyasa
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Ƴan Najeriya za su fara aiki a ƙasashen ƙetare ta hanyar intanet

Siyasa

Ƴan Najeriya za su fara aiki a ƙasashen ƙetare ta hanyar intanet

Bello Sani November 13, 2020 8


Background
share close

Hukumar bunkasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa NITDA, Kashifu Inuwa Abdullahi ya bayyana cewa ƴan Najeriya za su fara aiki a ƙasashen ƙetare ta hanyar Intanet, kamar yadda jaridar Daily Nigeria ta rawaito

“Akwai tsarin da mu ka fitar a kwanan nan wanda ƴan ƙasa za su ci gajiyarsa. Tsari ne wanda za su iya samun aiki a wata ƙasa su kuma gabatar da shi alhalin su na nan Najeriya wajen amfani da yanar gizo.

Mun zo da wannan tsarin ne saboda mun ga kamar ƙasar Indiya ce ta mamaye wannan bangaren kasuwanci a Duniya, sai mu ka ga ai Najeriya mun ma fi ƙasar Indiya dama idan za a yi.

Na farko, lokacin mu ya fi kusa da ƙasar Amurka da Turai akan lokacin Indiya. Na biyu, Najeriya mun fi mutanen da su ka iya turanci, saboda yanzu a ƙasar Indiya wadanda su ka iya turancin ma raguwa su ke, saboda haka muka fitar da tsarin yadda Najeriya za ta mori wannan tsari”.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *