play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Addini
  • keyboard_arrow_right Duniya
  • keyboard_arrow_right Ƙasar Faransa na shirin kai sumame masallatan da ke angiza tsatsauran ra’ayi

Addini

Ƙasar Faransa na shirin kai sumame masallatan da ke angiza tsatsauran ra’ayi

Bello Sani December 3, 2020 15


Background
share close

Ministan cikin gida na Faransa ya ce gwamnatin ƙasar za ta ƙaddamar da wani gagarumin shiri da ba a taɓa ganin irinsa ba kan masallatan da ake zargi na karfafa tsatsauran ra’ayin addinin Islama.

Mista Gerald Darmanin ya ce za a fara ne da masallatai 76 a cikin kwanaki masu zuwa, wataƙila ma a rufe wasunsu idan ta kama.

Wannan dai shi ne sabon matakin da gwamnatin shugaba Emmanuel Macron ta dauka bayan hare-haren da ke da alaƙa da na masu tsatsauran ra’ayi a kasar.

A kwanakin baya ne aka fille kan malamin da ya nuna wa ‘yan ajinsa zanen Annabi Muhammad, wanda ake kallo a matsayin izgilanci ga addinin Islama da mabiyansa.

Zane-zanen da wasu Faransawa ke yi tare da alaƙantasu da wani addini na ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce a duniya, har ta kai ga ƙasashen Musulmai ƙauracewa kayan da Faransan ke samarwa.

A kwanan baya ne shugaba Emmanuel Macron ya nemi shugabannin Musulmai da su amince da abin da ya kira “tsarin mulkin Jamhuriyya” a wani ɓangare na yaƙar masu tsaurin kishin addinin Islama.

Dokar ta bayyana cewa Musulunci addini ne ba wata manufar siyasa ba, tare da haramta “katsalandan daga ƙasashen waje” a ƙungiyoyin Musulmi.

Mista Macron ya kuma kare tsarin manufofin Faransa bayan hare-haren da aka kai da suka ƙunshi har da fille kan malamin da ya nuna wa ɗalibai zanen ɓatanci ga Annabi Muhammad a aji a watan jiya.

“Wasu sharuɗɗa za a rubuta su cikin launin baƙi da fari (cikin kundin): wato ƙin amincewa da manufar siyasa a addinin Musulunci da kuma duk wani katsalandan daga wata ƙasa,” kamar yadda wata majiya ta shaida wa jaridar Le Parisien bayan ganawar.

Wakilan majalisar Musulman ta CFCM sun kuma amince da kirkirar Majalisar Limamai ta Kasa, wadda za ta tantance malaman da ba su shaida a hukumance, wanda kuma za a iya janyewa idan an saɓa sharuɗɗan

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *