play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Tattalin Arziki
  • keyboard_arrow_right Uncategorized
  • keyboard_arrow_right Ƙarin farashin fetur: NLC ta lashi takobin durƙusar da al’amura a 2022

Tattalin Arziki

Ƙarin farashin fetur: NLC ta lashi takobin durƙusar da al’amura a 2022

Bello Sani January 1, 2022 39


Background
share close

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta dage cewa ma’aikata da talakawa ba za su sake amincewa da karin farashin man fetur da gwamnatin kasar ke shirin yi ba.

A sakonsa na barka da arziƙin shigowa sabuwar shekara, shugaban kungiyar ta NLC Ayuba Wabba ya ce har yanzu gwamnati ba ta ja da baya a kan aniyar ta ta ba.

‘’To, kungiyar kwadago ta bayyana matsayinta a kan wannan batu. Mun shaida wa gwamnati a fili cewa ƴan Najeriya sun sha wahala sosai kuma ba za su sake jure irin wannan ba’’ inji shi.

NLC dai ta ce a shirye take ta durƙusar da al’amura cik a Najeriya matsawar gwamnati ta sake bijiro da wannan batu.

.

Rate it
Previous episode
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *