
Sarkin Kano Aminu Ado Bayero: Babban burina a rayuwa ya cika
Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce babban burinsa a rayuwa shi ne ya gaji magabatansa kuma yanzu hakan ya tabbata. Cikin wannan hira ta musamman da ya yi […]
Tarihin Garin Kadawa
Bello Sani
Sarkin Noman Daura Bello Sani
Masarautar Daura Bello Sani
Sauraremu Kai Tsaye Bello Sani
Wani jigo a jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ya bayyana cewa babu wata jam’iyya da tsarin karɓa-karɓa zai fidda ita a zaɓen shekara ta 2023 – batun da ke ci gaba da ɗaukan hankalin jama’a da ma ƴan siyasar ƙasar.
Har yanzu dai jam`iyyar APC mai mulki ba ta bayyana shiyyar da za ta bai wa takarar shugabancin kasar ba.
Alhaji Isa Tafida Mafindi wanda jigo ne a APC ya shaida wa BBC cewa wajibi ne jam`iyya ta ba da fifiko ga cancanta, idan tana so ta kai bantenta a shekarar 2023.
Da yake tsokaci kan batun miƙa mulkiKudancin Najeriya kuwa, Mafindi ya bayyana cewa “zamanin Jonathan Arewa ta yi wa Kudu kara, Arewa ta danne zuciya, da aka ce a haɗu a yi, ai raba ƙafa suka yi Kudu maso Yamma,
inda Buhari bai samo ƙuri’u da ya samu daga Borno da Kano da Katsina da Kaduna da sauransu ba. da tuni sun hade da abokanansu suna mana gwalo”. in ji shi.
Mafindi ya ce a ra’ayinsa, yana ganin mutumin da ya fi dacewa ya shugabanci ƙasar shi ne ɗan Najeriya da bai kai shekara 60 ba da haihuwa.
“A dubi wa zai sarrafa mana nama ya fidda ita da manta daga wuta, muna da irin waɗan nan haziƙan samari suna ko ina”. in ji jigon.
Ya ƙara da cewa ba ya goyon bayan shiyya saboda a ganinsa biyan buƙatun ƴan Najeriya kuma ya kasance an sa Najeriya a gaba shi ne abu na farko da ya kamata a fi mai da hankali a kai.
Masharhanta dai na yi wa al’amarin karba-karba kallon wani abu da ‘yan kasar suka kirkira ba don yana cikin tsarin mulkin kasar ba.
Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce babban burinsa a rayuwa shi ne ya gaji magabatansa kuma yanzu hakan ya tabbata. Cikin wannan hira ta musamman da ya yi […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)