
Aisha Buhari ta rufe shafinta na Twitter
Mai dakin shugaban Najeriya Aisha Buhari ta rufe shafinta na Twitter jim kadan bayan sanarwar da gwamnatin kasar ta fitar ta dakatar da shafin a Najeriya a yammacin ranar Juma’a. […]
Tarihin Garin Kadawa
Bello Sani
Sarkin Noman Daura Bello Sani
Masarautar Daura Bello Sani
Sauraremu Kai Tsaye Bello Sani
Rundunar ‘yansada Jihar Kebbi ta tabbatar da mutuwar mutum 66 a karamar hukumar Danko-Wasagu tare da cewa ana fargabar adadin zai iya wuce haka.
Kakakin rundunar ‘yansanda na Jihar DSP Nafi’u Abubakar ne ya bayyana wa BBC hakan yana cewa harin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin karfe 3 na rana, a kauyuka takwas na karamar hukumar.
A cewar kakakin kauyukan sun hada da Kimpi da koro da Dimi da Zutu da Rafin Gora da Iguenge.
Yace harin ya fi shafar manyan maza sai kuma mata, amma har yanzu ba su kai ga tantance adadin matan da abin ya rutsa da su ba.
Ko a watan jiya sai da ‘yan bindiga suka farwa karamar hukumar suka kashe ‘yan sanda tara cikin har da DOP yankin.
Mai dakin shugaban Najeriya Aisha Buhari ta rufe shafinta na Twitter jim kadan bayan sanarwar da gwamnatin kasar ta fitar ta dakatar da shafin a Najeriya a yammacin ranar Juma’a. […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)