play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Shariah
  • keyboard_arrow_right Waiwaye: An tsayar da ranar yanke wa Zakzaky hukunci

Labarai

Waiwaye: An tsayar da ranar yanke wa Zakzaky hukunci

Bello Sani July 4, 2021 3


Background
share close

Kotu ta tsayar da ranar shari’ar Zakzaky

A ranar Laraba da ta gabata wata babbar kotun jiha a Kadunan Najeriya ta tsayar da ranar yanke wa Sheikh Ibrahim Zakzaky da mai dakinsa Malama Zinat hukunci.

Kotun ta tsayar da ranar 28 ga wannan watan na Yuli domin yanke wa jagoran ƙungiyar ƴan shi’a ta IMN

Gwamnatin jihar Kaduna ce ta gurfanar da su a gaban kotun kan tuhume-tuhume da dama ciki har da aikata kisan kai da gangan da gudanar da taro ba bisa ƙa’ida ba.

Lauyoyin Sheikh Ibrahim Zakzaky bisa jagorancin Femi Falana, sun gabatar wa da kotun buƙatar ta yi watsi da ƙarar saboda a cewarsu an gaza tabbatar da tuhume-tuhumen, ko da yake lauyoyin da suke ƙara sun buƙaci kotun ta ci gaba da shari’ar la’akari da shaidun da suka gabatar.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *