
Yanzun nan: Tashin hankali yayin da majalisa ta yi watsi da dokar zabe ta Buhari
Majalisar Dattawa ta yi watsi da kudurin dokar zabe da shugaba Buhari ya gabatar saboda wasu dalilai A baya majalisar ta fusata da jin yadda kotu ta ba da umarni […]
Tarihin Garin Kadawa
Bello Sani
Sarkin Noman Daura Bello Sani
Masarautar Daura Bello Sani
Sauraremu Kai Tsaye Bello Sani
Kebbi – Tsagerun yan bindiga sun farmaki jerin gwanon motocin mataimakin gwamna jihar Kebbi, Samaila Yombe, ranar Talata da daddare.
Vanguard ta tattaro cewa yan ta’addan kai wa tawgaar mataimakin gwamnan hari ne tsakiyar kauyen Kanya da misalin ƙarfe 8:00 na dare.
A cewar sakataren watsa labarai na mataimakin gwamnan, Abdullahi Yalmo, waɓda ya tabbatr da faruwar lamarin, ya ce jami’in ɗan sanda ASP Idris Umar Libata, ya rasa rayuwarsa.
Ya ce ɗan sandan ya rasa rayuwarsa ne yayin d asuka tarbi yan bindigan, suka yi musayar wuta tsakanin su.
Yalmo ya yi bayanin cewa uban gidanasa tare da rakiyar kwamandan barikin sojojin Najeriya dake Zuru domin zuwa ta’aziyya da jaje ga iyalan mutanen kauyen Kanya.
Mataimakin gwamnan yaje ta’aziyya ne biyo bayan wani mummunan lamarin da ya faru da harin yna bindiga, wanda ya lakume rayukan aƙalla yan Bijilanti 68, da kuma wasu fararen hula da dama.
Sakataren watsa labaran mataimamin gwamnan yace:
“Allah ya tseratar da Uban gidan mu, amma bisa rashin sa’a ya yi rashin ɗaya daga ciki haziƙan yan sandan dake tare da shi.”
Da aka tuntubi kakakin hukumar yan sanda reshen jihr Kebbi, SP Nafiu Abubakar, bai ɗaga kiran wayar da aka jera masa ba domin tabbatar da abin da ya auku.
Majalisar Dattawa ta yi watsi da kudurin dokar zabe da shugaba Buhari ya gabatar saboda wasu dalilai A baya majalisar ta fusata da jin yadda kotu ta ba da umarni […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)