
Yadda ‘yan bindiga suka kashe ‘yan sa kai 63 a Kebbi
An gudanar da jana’izar kimanin mutum 60 da suka rasa rayukansu sanadiyyar wani harin kwanton ɓauna da ƴan bindiga suka kai wa ƴan sa kai a yankin Zuru da ke […]
Tarihin Garin Kadawa
Bello Sani
Sarkin Noman Daura Bello Sani
Masarautar Daura Bello Sani
Sauraremu Kai Tsaye Bello Sani
FCT, Abuja – Babban kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Talata, a kori Gwamna David Umahi na Jihar Ebonyi da Mataimakinsa Dr Eric Kelechi Igwe, bayan sun fice daga jam’iyyar PDP sun koma APC mai mulkin sa, rahoton Vanguard.
Kotun, a hukuncin da Mai sharia Inyang Ekwo, ya yi, ta ce kuri’u 393,042 da Gwamna Umahi ya samu a zaben ranar 6 ga watan Mari na gwamnan Jihar Ebonyi, na jam’iyyar PDP ne kuma doka bata amince a mayarwa APC ba.
A cewar kotun, bayan komawa jam’iyyar APC, Umahi da mataimakinsa, ba PDP kadai suka bari ba, sun raba kansu da kuri’u jam’iyyar ta PDP, Daily Trust ta rahoto.
Kotun ta ce idan aka yi la’akari da sakamakon zaben na gwamna, kujerar gwamnan Jihar Ebonyi da mataimakinsa, ‘mallakar wanda suka yi karar ne ba wata jam’iyyar daban ba.’
“Babu wani tanadi a kundin tsarin mulkin kasa da ya nuna ana iya musayar kuri’u daga jam’iyya daya zuwa wata jam’iyyar.”
Ta ce jam’iyyar PDP ce ke da kuri’un da kujerun da masu zabe a Jihar Ebonyi suka kada, don haka ba za a iya mika wa Gwamna Umahi da mataimkinsa kuri’un ba idan sun fice daga jam’iyyar.
Don haka kotun ta bada umurnin cewa nan take Dave Umahi da Igwe su ajiye mukamansu.
Ta kuma umurci hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta karbi sunayen mutanen za su maye gurbin Umahi da mataimakinsa daga PDP, ko kuma ta sake yin sabon zabe a jihar Ebonyi kamar yadda sashi na 177(c) na kundin tsarin mulki da aka yi wa kwaskwarima ya ce.
Kotun ta kuma hana Umahi da mataimakinsa Igwe cigaba da amsa sunan gwamna da mataimakinsa na jihar Ebonyi.
Kotun ta yanke hukuncin ne bayan karar da jam’iyyar PDP ta shigar bayan Umahi da mataimakinsa sun koma APC. Saurari karin bayani……..
An gudanar da jana’izar kimanin mutum 60 da suka rasa rayukansu sanadiyyar wani harin kwanton ɓauna da ƴan bindiga suka kai wa ƴan sa kai a yankin Zuru da ke […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)