
Babu kan ta: Kwamishinan Ganduje, Shugabannin kananan hukumomi sun je hannun DSS
A ranar Larabar nan ne DSS ta damke wasu shugabannin kananan hukumomi biyu na jihar Kano Ana zargin wasu manyan ‘yan siyasa da hannu a rikicin siyasan da ya jawo […]
Tarihin Garin Kadawa
Bello Sani
Sarkin Noman Daura Bello Sani
Masarautar Daura Bello Sani
Sauraremu Kai Tsaye Bello Sani
Bashir Sani March 9, 2022 10
Abuja – Majalisar dattawa ta tabbatar da zababbun kwamishinonin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC.
Majalisar ta tabbatar da su ne a ranar Laraba, 9 ga watan Maris, bayan duba rahoton kwamitin majalisar kan yaki da rashawa da laifukan da suka shafi kudi, jaridar Punch ta rahoto.
Sabbin kwamishinonin da aka tabbatar sun hada da:
1. Sanata Anthony Agbo
2. Anne Otelafu Odey
3. Alhaji Goni Ali Gujba
4. Dr. Louis Solomon Mandama
5. Olugbenga Adeyanju AIG (mai ritaya).
A jawabinsa, shugaban kwamitin, Sanata Suleiman Abdu Kwari, ya tuna cewa shugaba Buhari ya janye sunan daya daga cikin zababbun kwamishinonin, Misis Mojisola Yaya-Kolade sannan ya maye gurbinta da Olugbenga Adeyanju AIG (mai ritaya), wanda kwamitin ya tantance.
Ya bayyana cewa zababbun kwamishinonin sun bayar da amsa yadda ya kamata yayin amsa tambayoyin kwamitin kan yadda za su cika aikin hukumar.
Ya kara da cewa, bayan bincikar takardunsu, kwamitin ya gamsu da cewa wadanda aka zaba suna da kwarewa, mutunci kuma za su iya sauke ayyukan da aka zabe su suyi.
Ya kuma bayyana cewa, babu wani rahoto na tsaro ko korafe-korafe da aka yi kan wani daga cikin wadanda aka nada.
Bashir Sani March 9, 2022
A ranar Larabar nan ne DSS ta damke wasu shugabannin kananan hukumomi biyu na jihar Kano Ana zargin wasu manyan ‘yan siyasa da hannu a rikicin siyasan da ya jawo […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)