play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right Shariah
  • keyboard_arrow_right Sheikh Abduljabbar ya nemi afuwa cewa ba a ‘fahimce ni ba’

Labarai

Sheikh Abduljabbar ya nemi afuwa cewa ba a ‘fahimce ni ba’

Bello Sani July 11, 2021 12


Background
share close

Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara ya nemi afuwar al’umar Musulmi game da kalaman ɓatanci ga Annabi Muhammadu SAW da ake zarginsa da yi yana mai cewa “ba a fahimce ni ba” ne.Kipp

Cikin wani saƙon sauti, an ji malamin na cewa “idan har waɗannan kalamai daga ni suke, ƙirƙirarsu na yi, babu su a litattafai to lallai ya isa babban laifi da ya wajaba a gare ni da na gaggauta tuba”.

Ya ƙara da cewa: “Amma idan ba daga ni ba ne, daga cikin wsaɗncen litattafai ne, to wannan kuma ya zama wani abu daban. Sai mu yi roƙon Allah ya haska wa al’umma su tashi tsaye mu taimaki addininmu, mu fitar da hadisan ƙarya daga ciki domin gudun kar a rusa mana addinin da su.”

BBC Hausa ta fahimci cewa shehin malamin ya nemi afuwar ce bayan wasu ɗalibansa sun nemi ya yi hakan.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *