
Masarautar Katsina ta dakatar da bikin hawan Sallah a bana
Sarkin Katsina ya kashe bukukuwan hawan sallah a wannan shekara. Abdulmumin Kabiru Usman ya bayyana wannan a wata sanarwa jiya. Mai martaba ya ce za ayi amfani da lokacin wajen […]
Tarihin Garin Kadawa
Bello Sani
Sarkin Noman Daura Bello Sani
Masarautar Daura Bello Sani
Sauraremu Kai Tsaye Bello Sani
Sanarwar kwamitin ganin wata a Najeriya ta bayyana cewa, ba a alamar watan Shawwal ba. An sanar cewa, gobe za a tashi da azumi na 30 domin cike watan Ramadanan bana da zai kai kwanaki 30. Daga sanarwar, a fahimci cewa, Alhamis, 13 ga watan Mayu za ta kasance ranar karamar sallah
Kwamitin Sarkin Musulmi kan harkokin addini tare da hadin gwiwar Kwamitin Duban Wata a Najeriya sun sanar da cewa ba su samu labarin ganin watan Shawwal a Najeriya ba a yau Talata 11 ga watan Mayun wanda ya yi dai-dai da 29 ga watan Ramadana.
Don haka Sarkin Musulmi, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar CFR, ya ayyana Alhamis 13 ga watan Mayu 2021 a matsayin ranar Sallah kuma 1 ga watan Shawwal.
Sarkin Musulmi ya taya Musulmin Najeriya murna tare da fatan Allah ya yi masu albarka.
Sanar da Legit.ng Hausa ta gano a shafin kwamitin na Tuwita ya karanta: “Babu alamar ganin watan Shawwal a Najeriya yau Talata 11 ga Mayu, gobe Laraba 12 ga Mayu shi ne 30 ga Ramadan. Nan gaba kadan za a fitar da wata sanarwa a hukumance daga majalisar.
A wani labarin, A yau 11 ga watan Mayu ne aka cika kwanaki 29 ana azumtar watan Ramadana mai alfarma, kuma ake sa ran ganin watan Shawwal domin ajiye azumin tare da fara bikin karamar Sallah.
Mun kawo muku jerin kasashen da suka sanar da yin azumi 30, wato sallah karama a wadannan kasashen sai ranar Alhamis 13 ga watan Mayu 2021, kamar yadda BBC Hausa ta ruwaito.
Sarkin Katsina ya kashe bukukuwan hawan sallah a wannan shekara. Abdulmumin Kabiru Usman ya bayyana wannan a wata sanarwa jiya. Mai martaba ya ce za ayi amfani da lokacin wajen […]
Copyright Matasa Radio - by Bello Sani
Post comments (0)