play_arrow

keyboard_arrow_right

skip_previous play_arrow skip_next
00:00 00:00
playlist_play chevron_left
volume_up
chevron_left
  • Home
  • keyboard_arrow_right Tsaro
  • keyboard_arrow_right Labarai
  • keyboard_arrow_right An Kashe Jami’in Dan Sanda, An Kama Yan Shi’a 49 Bayan Sabon Zanga-zanga Da Aka Yi A Abuja

Tsaro

An Kashe Jami’in Dan Sanda, An Kama Yan Shi’a 49 Bayan Sabon Zanga-zanga Da Aka Yi A Abuja

Bello Sani May 9, 2021 18


Background
share close

Rundunar yan sanda ta sanar da rasa wani jami’inta sakamakon wata zanga-zangar yan shi’a a Abuja. Lamarin ya afku ne a ranar 7 ga watan Mayu wanda yayi daidai da tattakin da suke yi a ran Juma’ar karshe ta Ramadan

An kuma yi nasarar cafke ‘ya’yan kungiyar guda 49, sannan za a gurfanar da su da zaran an kammala bincike.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da kisan wani jami’inta, ASP Adama Ezekiel, yayin wata zanga-zangar da ‘yan kungiyar shi’a (IMN) suka yi.

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar FCT, Mariam Yusuf, mataimakiyar Sufeta ta ’yan sanda, ce ta sanar da mutuwar Ezekiel a cikin wata sanarwa, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Rate it
Previous post
Post comments (0)

Leave a reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *